1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan Aljeriya ba sa so Bouteflika ya zarce

Mouhamadou Awal Balarabe
March 1, 2019

Jami'an tsaro sun yi amfani da karfi wajen tarwatsa 'yan Aljeriya da ke zanga-zangar adawa da sake takarar shugaban kasar Abdelaziz Bouteflika da ke neman wa'adin mulki na biyar

https://p.dw.com/p/3ELDg
Algerien Proteste gegen die Regierung
Hoto: picture-alliance/AP Photo/F. Gudoum

'Yan sandan kasar Aljeriya sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa 'yan kasar da suka mamaye kofar ofoshin Firaminista don nuna adawa da neman wa'adi na biyar na mulki da shugaban Abdelaziz Bouteflika ya yi. Ba a dai bayyana ko wadanda ke neman tserewa sun ji rauni ko sun yi asarar rayuka ba. Sai dai Kamfanin dillanacin labaran Faransa na AFP ya ruwaito cewa dubban 'yan Aljeriya sun fantsama kan titunan Algiers da wasu garuruwan kasar don nuna adawa da manufofin gwamnatin da ke ci a yanzu.

Tun a ranar 10 ga watan Fabirairu ne Bouteflika ya bayyana aniyar sake tsayawa takara a zaben shugaban kasar da zai gudana a ranar 19 ga watan Afirilu, duk da shanyenwar barin jiki da yake fama da shi. Ranar Lahadi ce ranar karshe da doka ta amince ta ajiye takardun takara a gaban kotun tsarin mulki.