1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kenya: Ruto ya yi kiran da a zauna lafiya

Abdourahamane Hassane
August 16, 2022

A Kenya kwana daya bayan da hukumar zabe ta ayyana William Ruto a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da kishi 50,49 yayin abokin hamayyarsa Rail Odinga ke da kishi 48 da ya ka.

https://p.dw.com/p/4Fa2v
Kenia Nairobi | William Ruto gewinnt Präsidentschaftswahl
Hoto: TONY KARUMBA/AFP/Getty Images

 

Sabon shugaban Kenya yayi kira ga al'umma da su kwantar da hankula sa'annan ya sha alwashin yin aiki domin gina kasarsa "Ina so in yi wa al'ummar Kenya alkawarin cewar, zan gudanar da mulkin dimukaradiyya cikin haske da adalci, za mu yi aiki tare da 'yan adawa ta yada za su iya saka ido a kan yadda muke tafiyar da mulki. Kafin bayyana sakamakon zaben hudu daga cikin manbobi bakwai na hukumar zaben sun nisanta kansu daga sakamakon. An samu barkewar zanga-zanga a Kisumu da ke a yankin arewacin kasar ta Kenya da kuma yankunan da ke kusa da Nairobi babban birnin kasar jim kadan bayan bayyana sakamakon zaben da magoyan bayan Raila Odinga suka yi zargin cewar an tafka magudi.