1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

WHO ta sake gargadi kan yaduwar Omicron

December 15, 2021

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ce sabon nau'in corona na Omicron na yaduwa cikin gaggawa a tsakanin jama'a, tana mai jan hankalin kasashen duniya game da hakan.

https://p.dw.com/p/44H9H
Schweiz Genf | WHO Direktor Tedros Adhanom Ghebreyesus
Hoto: Martial Trettini/KEYSTONE/picture alliance

Shugaban Hukumar ta WHO, Dr. Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce akwai kasashe 77 da cutar ke cikinsu, kuma akwai yiwuwar sun shige cikin tarin wasu kasashe da ba a iya tantance su ba har yanzu.

Omicron wanda da farko ya bulla a kasar Afirka ta Kudu, na saurin rikida abin kuma da yake kada hankalin masana kimiyyar lafiya a duniya.

Amirka wacce coronar ta yi wa lahani, na da sama da mutum dubu 800 da ta halaka a cewar cibiyar bincike da ke jami'ar Johns Hopkins ta kasar.

Sanarwar hukumar ta WHO ta zo ne daidai lokacin da kamfanin harhada magungunan na Pfizer, ya ce rigakafin da ya samar na tasiri a kan Omicron din, duk da cewa bayanan farko sun nuna akasin hakan.