Wadanda suka mutu a Italiya sun karu
August 15, 2018Talla
'Yan sandan kasar ta Italiya sun ce akalla mutum 30 ne suka mutu, lokacin da babbar gadar da ke birnin Genoa ta rushe sakamakon ruwan sama mai karfi da aka tafka.
Motoci masu yawa ne dai suka fada daga tsawon mita 100 suka kuma sauka kan hanyar jirgin kasa da ke karkashin gadar.
Jami'an kwana-kwana na amfani da karnuka na musamman, don nemo mutane da ke sauran motsi ya zuwa wayewar garin wannan Laraba.
An dai yi ta jin kukan mutane da ke neman dauki, a karkashin buraguzai.