1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi Chaina da rikicin Hong-Kong

Gazali Abdou Tasawa MNA
August 20, 2019

Kamfanonin Twitter da na Facebook sun zargi gwamnatin kasar Chaina da yin amfani da shafukan sadarwarsu wajen bata suna da kuma rarraba kawunan masu zanga-zangar neman sauyi a Hong-Kong. 

https://p.dw.com/p/3OB0B
Hongkong Victoria Park Demonstration und Proteste
Hoto: picture-alliance/AP/Vincent Thian

A cikin wani sako da ya wallafa a ranar Litinin, kamfanin Twitter ya ce bayan bankado matsalar ya dakatar da aikin wasu shafukan Twitter 936 wadanda a bisa goyon bayan gwamnatin Chaina ke aiki tare wajen yin farfagandar kawo goyon baya ga gwamnatin Hong-Kong, baya ga wasu da dama shafukan na Twitter sama da dubu 200 na kasar ta Chaina da ya dakatar da aikinsu. 

Shi ma dai daga nashi bangare kamfanin Facebook ya sanar da shafe bayanan da ke cikin wasu shafukan sadarwar na Facebook na wasu mutanen da ke da alaka da gwamnatin ta Bejin, baya ga wasu shafukan sama da dubu 15 da ya shafe a baya.

Sai dai kamfanonin biyu ba su bayyana tasirin da matakin nasu ya yi ba wajen rage kaifin farfagandar da Chainar ke yi wajen rarraba kawunan masu zanga-zangar neman sauyin na Hong-Kong.