1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan gudun hijirar Bama na cikin tasku

Lateefa Mustapha Ja'afarMay 15, 2015

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ya ce ya damu matuka da rahotanni da ke nuni da cewa wasu kasashe sun hana daruruwan 'yan gudun hijirar Bama shiga kasashensu.

https://p.dw.com/p/1FQPA
Halin da Musulmin Rohingya da ke gudun hijira ke ciki
Halin da Musulmin Rohingya da ke gudun hijira ke cikiHoto: picture-alliance/dpa

Sama da Musulmin Rohingya da ke gudun hijira da ga kasar ta Bama 1,000 da suka tserewa kashe su da mabiya addinin Buda ke yi a kasarsu ne ke cikin halin tasku da ya hadar da yunwa da kishirwa da kuma rashin koshin lafiya ke neman mafaka, inda rahotanni ke nuni da cewa kasar Bangaladash da sauran kasashen yankin kudancin Asiya sun koresu tare da hanasu shiga kasarsu. Ban ya bukaci gwamnatocin yankin kudancin na Asiya da su bar tashoshin jiragen ruwansu a bude kana su basu damar shiga domin samun taimakon gaggawa da suke bukata.