Taron ministocin tsaro na kasashen Sahel
January 15, 2018Talla
Yunkurin na magance ta'addanci da sauran muggan laifuka ya hada kasashen Burkina Faso da Chadi da Mali da Mauritania da kuma Jamhuriyar Nijar wadanda zasu hada gwiwa don kirkirar wata rundunar tsaro mai dakaru 5000 kafin tsakiyar shekarar 2018 don magance ta'addanci da dangoginsa a yankin.
Wadannan kasashe sun yi fama da hare-haren da suka samo asali daga Najeriya wanda ya yi sanadiyyar rasa dubban rayuka tare da raba mutane da muhallansu abinda yayi sandaiyyar gurgunta tattalin arzikin kasar da kuma haifar da matsananciyar yunwa.
Rundunar ta G5 Sahel ana sa ran za ta yi aiki tare da dakarun Faransa da kuma Jami'an kwantar da tarzoma dubu 12 na MINUSMA da ke aiki a kasar Mali.