Taba Ka Lashe: 17.01.2018
January 19, 2018Talla
Sau da yawa ana yi wa 'yan gudun hijira da bakin haure kallon masu cin amfanin ayyukan agaji da tallafin da ake ba su, ba safai ne ake la'akari da irin gudunmawar da suke bayarwa a cikin al'ummomin da suke zaune a cikinsu ba. A wani yanki na kasar Girika wasu kiristoci bakin haure daga Afirka sun taimaka an farfado da wata majami'a da kusan ta zama kango, ba a kuma zuwa ibada a ciki.