1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojoji za su tsananta bincike a Najeriya

September 22, 2019

Sojoji a Najeriya, sun ce za su fara tsananta bincike a kan matafiya a jihohin arewa maso gabashin kasar, inda za a bukaci kowane matafiyi ya nuna katin shaida saboda dalilai na tsaro.

https://p.dw.com/p/3Q3hl
Civilian Joint Task Force CJTF Nigeria Boko Haram
Hoto: AFP/Getty Images/F. Plaucheur

A cewar sojojin yin hakan ya wajaba ne saboda sahihan bayanan da suke da su na cewar a yanzu mayakan kungiyoyin Boko Haram din nan biyu, suna sajewa da jama'a a cikin garuruwan yankin bayan fatattakarsu da ake yi a dazuka.

Jihohin Adamawa da Borno da kuma Yobe ne matakin zai shafa, inda matafiya zasu rika tafiya da takardun da za su tabbatar da shaida a kansu.

Sanarwar da rundunar sojin ta fitar a wannan Lahadi, ta ce duk wani da aka samu ba shaida, zai fuskanci binciken kwa-kwaf da zai tabbatar da alakarsa ko kuma akasi da ayyukan ta'addanci.

A makon jiya ne dai, dakarun Najeriyar suka dakatar da ayyukan kungiyar agajin nan ta Action Against Hunger a shiyar, saboda zarginta da taimaka wa mayakan Boko Haram da abinci da magunguna.