1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabannin za su hadu a Masar a kan Zirin Gaza

October 12, 2025

Shugabanni kasashen duniya na shirye-shiryen babban taron koli kan zaman lafiyar Zirin Gaza, wanda zai gudana a kasar Masar. Taron haka nan yana da burin duba wasu matsalolin yankin Gabas ta Tsakiya

https://p.dw.com/p/51rHO
Masar, Alkahira 2025 | Abdel Fattah al-Sisi ya gana da jakadan Amurka na Gabas ta Tsakiya, Steve Witkoff.
Masar, Alkahira 2025 | Abdel Fattah al-Sisi ya gana da jakadan Amurka na Gabas ta Tsakiya, Steve Witkoff.Hoto: Egyptian Presidency/UPI Photo/IMAGO

Shugabanni daga sassan duniya na shirye-shiryen halartar babban taron koli kan zaman lafiyar Zirin Gaza, wanda zai gudana a ranar Litinin a birnin Sharm el-Sheikh, na tekun Bahar Maliya na Masar.

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi da shugaban Amurka Donald Trump, su ne za su jagoranci taron.

Shugabanni sama da ashirin daga kasashe daban-daban ne ake sa ran halartarsu, ciki har da Sakataren Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, da Firaministan Burtaniya Keir Starmer da takwaransa ta Italiya Giorgia Meloni da ma Pedro Sanchez na Spain.

Sauran mahalarta sun hada da Shugaban Faransa Emmanuel Macron, Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, Sarkin Jordan Abdullah na II, da wakilin Tarayyar Turai Antonio Costa.

Fadar shugaban kasa Masar ta ce manufar taron ita ce kawo karshen yakin Gaza, da karfafa yunkurin samar da kwanciyar hankali a yankin Gabashin Tsakiya.