Shirin tsagaita wutar Siriya ya fara aiki
October 26, 2012Da ya ke magana game da shirin na tsagaita wuta na tsawon kwanaki huɗu, shugaba hukumar kare haƙƙin bani adama nan ta Syrian Observatory for Human Rights da ke da mazauninta a birnin London na Burtaniya, Rami Abdel Rahman ya ce kawo yanzu dai ba su ga alamaun keta wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta ba.
A nasu ɓangaren, dakarun gwamnatin Assad sun ce za su mutunta yarjejeniyar to amma fa shakka babu za su maida martani muddin ɓangaren 'yan tawayen su ka keta dokar da aka gindaya.
A farkon wannan makon da mu ke cikin ne dai manzon musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya da ƙasahsen larabawa kan rikicin na Siriya Lakhdar Brahimi ya shawarci ɓangarorin biyu da su amince da shirin na tsagaita wuta albarkacin Idin babbar Sallah, kana a yi amfani da damar wajen tattaunawa da nufin wanzar da zaman lafiya a ƙasar.
Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Mohammed Awal Balarabe