Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
Za a ji yadda talakawa ke kukan tsadar wutar lantarki a kasar Masar.
A karon farko cikin shekaru sama da 10, firaiministan Isra'ila Naftali Bennett ya gana da Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi, inda suka tattauna batun inganta hulda da juna da sasanta rikicin Faladsinawa da Hamas.
Wasu majiyoyi sun ce wutar lantarki ce sanadin tashin gobarar a lokacin da mutane akalla 5,000 ke addu'a a majami'ar a ranar Lahadi. Gwamnati ta kaddamar da bincike don gano tushen gobarar.
Masu gabatar da kara a Masar, sun kama mutane uku kan laifin tika rawa da waka a cikin masallaci bayan da aka wallafa a bidiyon a shafukan sad azumunta na yanar gizo.
A wannan Lahadin ce aka bude gasar cin kofin duniya ta kwallon kafa a kasar Qatar, inda aka fara taka leda tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Qatar da kuma ta kasar Ecuador.