1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan ta fara samun Tallafi daga Saudiya

Binta Aliyu Zurmi
August 7, 2019

Kasashen Saudiya da Hadadiyar Daular Larabawa sun yi alkawarin tallafawa kasar Sudan da kudi bayan tallafin tan dubu 540 na alkama da suka soma mikawa kasar da ke fama da rikici bayan juyin mulki.

https://p.dw.com/p/3NWit
Unruhen im Sudan | Demonstration
Hoto: picture-alliance/Xinhua/M. Khidir

Baya ga haka, kasashen biyu, sun ce akwai tsabar kudi na dala miliyan 500 da suka adana a babban  bankin Kasar Sudan, don daukar dawainiyar kayayyakin masarufi da zummar rage radaddin da jama'ar da ke cikin bukatar taimako za su amfana. Sudan dai ta kwashi watannnin tana fama da rikici kan samar da gwamnatin hadaka, bayan kifar da gwamnatin Oumar al-Bashir na kusan shekaru talatin.