1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Inganta yaki da ta'addanci a Sahel

Gazali Abdou Tasawa
November 13, 2019

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya sanar da shirin daukar sabbin matakan yaki da ta'addanci a yankin Sahel da aikawa da karin sojoji a yankin nan da 'yan makonni masu zuwa.

https://p.dw.com/p/3Sw8h
Mali Gao - G5-Staaten planen neue Eingreiftruppe in der Sahelzone
Hoto: picture-alliance/dpa/B. Pedersen

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya bayyana hakan ne lokacin da yake karbar bakuncin shugabannin kasashen Chadi da Nijar da kuma Mali a jiya Talata a fadar Elysee inda ya ce za a sake bayyana takamaiman aikin rundunar Barkhan ta sojojin Faransa a yankin Sahel da kuma karfafa ta.

 A lokacin wannan haduwa dai shugabannin kasashen na Nijar da Mali da Chadi sun bayyana damuwarsu kan matsayin birnin Kidal wanda har ya zuwa yanzu gwamnatin Mali ba ta da iko a cikinsa, sannan sun nuna rashin jin dadinsu kan yadda kasashen duniya suka kasa cika alkawarin da suka dauka na tallafawa kasashen na Sahel a yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda.

Sai dai Shugaba Macron ya sha alwashin yin kira ga kasashen da suka yi alkawari kan su mutunta shi, sannan ya bayyana cewa za a samu karin sojoji a yankin zuwa karshen wannan shekara ko kuma farkon shekara mai kamawa.