1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rumbun boye makamai ya tarwatse a Iraki

Abdul-raheem Hassan
June 7, 2018

Fashewar ta haddasa asarar kayayyaki masu tarin yawa tare da lalata gidaje da manyan gine-gine da ke kusa da inda aka boye rokoki da wasu manyan makamai a birnin Bagadaza.

https://p.dw.com/p/2z3wZ
Irak Explosion in Bagdad
Hoto: Reuters/W. al-Okili

Hukumomin tsaro da likitoci a Iraki sun tabbatar da mutuwar mutane 16 tare da wasu 32 da suka jikata bayan fashewar abubuwa a wurin adana makamai kusa da unguwar 'yan shi'a a birnin Sadr d ake wani yanki na Bagadaza babban birnin kasar Iraki.

Rahotannin jami'an lafiya na cewa fashewar ta shafi mata da kananan yara, wani jami'an tsaro ya sheda wa kamfanin dillancin labarun AFP cewa, fashewar baya rasa nasaba da yawan manyan makamai da 'yan bindiga ke boyewa a tungarsu.