1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Sudan: Ruftawar mahakar zinare ta kashe mutane sama da 30

December 28, 2021

Wannan dai ba shi ne karon farko da aka samu hatsarin ba. A shekarun baya hukumomi sun taba rufe mahakar zinaren bayan wata ruftawa da ta yi. 

https://p.dw.com/p/44vxj
Abdalla Hamdok Ministerpräsident Sudan
Hoto: APTN

Kimanin mutane 31 ne suka mutu a yayin da wata mahakar zinare ta rufta a kasar Sudan. Ma'aikatar kula da albarkatun kasa ta sanar a dazu da rana cewa akwai karin wasu mutane takwas da suka samu munanan raunuka. Lamarin dai ya faru ne a garin Al-Nuhud da ke yamma da yankin Kordofan. 

Zinare dai na daga cikin hanyoyin da kasar ta Sudan da ke a gabashin Afirka ke samun kudin shiga. Sai dai galibin wuraren da ake hakar zinaren na aiki ba tare da sahalewar hukumomi ba.