1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin tawaye na neman sake barkewa a Chadi

Halimatu AbbasMarch 22, 2013

Wasu manya-manyan kungiyoyin 'yan tawaye da suka hada da UFR wadda ta ajiye makamai a shekara ta 2009 sun bada sanarwar sake daukar makamai domin yakar gwamnatin shugaba Idriss Deby Itno

https://p.dw.com/p/182Or
Hoto: Getty Images

Masu aiko da rahotanni sun bayyana cewar kungiyoyin sun yi wata ganawarsu ce a birnin Doha na kasar Qatar da nufin cimma matsaya guda domin kifar da shugaba Deby daga kan karagar mulkin kasar.

A shekara ta 2008 ne shugaban kasarya ketare rijiya da baya a lokacin da sojojin faransa suka taimaka masa korar 'yan tawayen daga fadarsa, to saidai a wannan karon gwamnatin Francois Hollande ta ce ko kusa baza ta saka hannunta ba a cikin rikicin cikin gidan Chadin ko da ya barke..Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar ya aika da kimanin dakarun kasar dubu biyu a kasar Mali domin yakar kungiyoyin kishin addini.

Mawallafi: Issouhou Mahamane
Edita: Halima Balaraba Abbas