1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Amirka da Koriya ta Arewa

March 29, 2013

Koriya ta Arewa ta ce ta girke na'urorin harba roka kazalika ta ce sojinta na cikin shirin ko ta kwana domin maida martani idan Amirka ta afka mata.

https://p.dw.com/p/186h1
epa03644058 A picture released by the North Korean Central News Agency (KCNA) on 29 March 2013 shows North Korean leader Kim Jong-un (sitting) convening an urgent operation meeting at 0:30 am on 29 March 2013 at an undisclosed location, in which he ordered strategic rocket forces to be on standby to strike US and South Korean targets at any time. Kim's order followed two US stealth bombers' first-ever drill over the Korean Peninsula the previous day. The North berated the drill as US hostility against it. EPA/KCNA SOUTH KOREA OUT NO SALES +++(c) dpa - Bildfunk+++ / Eingestellt von wa
Nordkorea / Kim Jong Un / MilitärsHoto: picture-alliance/dpa

Koriya ta Arewan dai ta ce mudin Amurka ta kai mata farmaki to ko shakka babu za ta maida martani ta hanyar kai harin ramuwar gayya a sansanonin sojin Amurkan da ke Koriya ta Kudu da Japan.A wata ganawa da ya yi da manyan hafsoshin sojin kasar, shugaban Koriya ta Arewan Kim Jong-un ya ce lokaci ya yi da za su rarrabe tsaki da tsaba da kasar ta Amirka.

Wannan shelar da Koriya ta Arewan ta yi dai ta biyo bayan shawagin da ta ce sojin Amurka sun yi a sararin samaniyar ta da jiragen yaki.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Halima Balaraba Abbas