1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikici na ci gaba a Sudan ta Kudu

Lateefa Mustapha Ja'afar
April 25, 2018

Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva Kiir ya yi watsi da kiraye-kirayen da 'yan adawar kasar ke masa na ya sauka daga kan karagar mulki.

https://p.dw.com/p/2weFh
Präsident der Republik Südsudan Salva Kiir Mayardit
Shugaban kasar Sudan ta Kudu Salva KiirHoto: imago/photothek/T. Koehler

'Yan adawar dai sun bayyana saukar ta Salva Kiir a matsayin wani bangare na kawo karshen yakin basasar da kasar ta kwashe tsahon shekaru hudu tana fama da shi. Kiir ya yi zargin cewa masu adawa da gwamnatinsa ne kawai ke kawo wasu bukatu da basu da tushe balle makama. An dai yi ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin basasar da ya barke tun a shekara ta 2013, sai dai tun ba a je ko ina ba yarjejeniyar ke rushewa a jaririyar kasar ta duniya.