1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Pekka Haavisto ya yi kira da a tsagaita bude wuta

April 15, 2026

Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya na musamman kan Sudan, Pekka Haavisto, ya yi kira da a tsagaita bude wuta. bayan fara yakin gwagwarmayar neman iko tsakanin Sojojin gwamnati karkashi da dakarun sa kai na RSF

https://p.dw.com/p/5CDv5
Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya na musamman kan Sudan, Pekka Haavisto
Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya na musamman kan Sudan, Pekka HaavistoHoto: Odd Andersen/AFP

Fiye da fararen hula 50,000 sun mutu a fadin kasar Sudan sakamakon yakin. Sama da 'yan kasar miliyan 14 sun yi hijira; lamarin da ya haifar da daya daga cikin matsalolin jin kai da gudun hijira mafi girma a duniya.

Yanzu haka dai masu bayar da agaji na taro a birnin Berlin fadar gwamnatin Jamus. Berlin din ta yi alkawarin dala miliyan 24 a bana, bayan Yuro miliyan 155 da ta bayar a bara.

Ana kuma tattauna yadda za a ci gaba da samar da tallafin gaggawa tare da bullo da sabbin dabarun sake zaman sulhu tare da tallafin Masar da Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa.