Pakistan: Turmutsitsi ya kashe mutane | Labarai | DW | 31.03.2023
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

Labarai

Pakistan: Turmutsitsi ya kashe mutane

Akalla mutane tara ne suka mutu a wani turmutsitsin da ya barke a birnin Karachi da ke kudancin Pakistan,yayin da jama'a suka garzaya zuwa wata masana'anta da aka shirya rabon sadaka na azumin Ramadan.

Turmutsitsin ya faru ne a lokacin da mata mabukata da ‘ya'yansu suka cincirindo a masanantar.inda cinkosso jama'a ya yi yawa.Yanhzu haka an kai gawarwakin mata shida da yara uku zuwa asibiti in ji kakakin 'yan sanda birnin na karashi Muhammad Farukh.