1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nyusi ya sake lashe zabe a Mozambik

October 28, 2019

An bayyana wanda ya lashe zaben shugaban kasar Mozambik da talakawan kasar suka zaba cikin makon da ya gabata. Hukumar zaben kasar ce dai ta sanar a hukumance.

https://p.dw.com/p/3S22w
Wahlen in Mosambik
Hoto: Getty Images/AFP/G. Guercia

An sake zaben Shugaba Filipe Nyusi na kasar Mozambik a karo na biyu, inda ya sami kashi 73% na kuri'un da aka kada, kamar dai yadda hukumar zaban kasar ta bayyana a yau Lahadi.

Alkaluman hukumar zaben sun ce abokin takararsa wanda tsohon jagoran kungiyar tawaye na Renamo ne, Ossufo Momade, ya sami kashi 22 na kuri'un.

An dai sa ran Shugaba Nyusin na jam'iyyar Frilimo ne dai zai yi nasara a zaben, sai dai ba da yawan kuri'un da aka sanar ba.

Zaben da aka yi a ranar 15 ga watan nan na Oktoba, ya kuma samar da 'yan majalisar kasa da kuma wasu wakilai na larduna.