Myanmar ta kare sojojinta daga zargi
August 29, 2018Talla
Majalisar Dinkin Duniya ta gabatar da jerin shedun laifukan take hakkin bil'adama da ake zargin sojojin Myanmar da aikatawa cikin har da fyade da muzgunawa musulmai bayan barkewar rikici a jihar Rakhine. Gwamnatin Myanmar ta ce sakamakon binciken ba shi da tuhse balle makama, sabaoda babu jami'a MDD da aka ba wa damar shiga kasar domin gudanar da bincike.