1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A na zargin 'yan jarida da bayar da bayanan sirrin kasa

Ramatu Garba Baba
July 9, 2018

Wata kotu a kasar Myanmar ta bayar da umarnin gurfanar da 'yan jaridan kamfanin dillancin labaran Reuters gaban kuliya don soma yi musu shari'a bisa zargin da a ke musu na bayar da wasu bayanan sirrin kasa.

https://p.dw.com/p/313Ua
Inhaftierte Journalisten in Myanmar
Hoto: Reuters/A. Wang

An zargi 'yan jaridan da aikata wannan laifi ne a lokacin da suke tura rahotannin labarin rikicin kabilanci yankin Rakhine na al'ummar 'yan Rohingya. 'Yan jaridan da suka hada da Wa Lone, mai shekaru talatin da biyu da Kyaw Soe Oo, mai shekaru ashirin da takwas  za su iya fuskantar hukuncin dauri na shekaru goma sha hudu muddun a ka tabbatar da laifin da a ke zarginsu a kai.

Mutanen biyu sun kwashi watannin bakwai a tsare a yayin da suke ci gaba da musanta laifin da a ke zarginsu da aikatawa.