1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane shida suka mutu a tekun Libiya

April 16, 2022

Hukumar kula da kauran jama'a ta duniya ta gano mutune shida da suka mutu a gabar ruwan Libiya.

https://p.dw.com/p/4A1uy
Mittelmeer Libyen | NGO Open Arms hilft Migranten im Holzboot
Hoto: Joan Mateu/AP/picture alliance

Hukumar kula da kauran jama'a ta duniya ta gano gawawakin wasu mutane 6 bayan da wani kwale-kwalen katako dauke da bakin haure kimanin 35 ya kife a gabar ruwan Libiya. Kawo yanzu dai ana ci gaba da neman wasu mutane 29 da suka yi batan dabo.

Ko a makon da ya gabata ma kimanin bakin haure 53 aka bayar da rahoton sun mutu a gabar ruwan Libiyan a cewar hukumar. Kasar Libiya da ta kwashe gomman shekaru ta na fama da rikici na zama matattara ta 'yan Afrika da nahiyar Asiya da ke son tsallakawa zuwa Turai ba bisa ka'ida ba.

Alkalumman Majalisar Dinkin Duniya na nuni da cewa kimanin bakin haure fiye da dubu 1 ne suka nutse a tekun Bahar rum a shekarar bara.