1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane da dama sun salwanta a Kwango

May 27, 2019

Wani hadarin jirgin ruwa ya yi sanadiyyar mutuwar wasu masu yawa a Kwango bayan faruwar irinsa a watan jiya da ya kashe mutum sama da 160 tare da batar wasu da dama.

https://p.dw.com/p/3J9lG
Kongo Rettungsaktion nach Bootsunglück auf Kiwusee 2015
Hoto: picture-alliance/AA/C. Kasereka

Akalla mutane 30 ne suka mutu yayin da wasu kimanin 200 kuwa suka bata a Jamhuriyar dimukuradiyyar Kwango, sakamakon nitsewar da wani jirgin ruwa ya yi. 

Lamarin ya faru ne a tafkin Mai-Ndombe da ke a yammacin kasar, a daren Asabar da ya gabata. 

Al'umar Kwangon dai sun fi amfani ne da sufurin ruwa, abin kuma da ya sanya yawaitar hadarin na ruwa a kasar.

Ana kuma danganta hakan da yawan daukar mutane da kayayyaki fiye da kima.

Kwararru sun ce daga cikin dalilan da ke sanya samun asarar rayuka a galibin haduran, sun hada ne da rashin amfani da rigunan kariya da kuma rashin kwarewa a harkar iyo.

Ko a watan jiya ma, an yi asarar rayukan mutum 167 a wasu haduran biyu dabam-dabam.