1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 1200 sun ƙaurace wa matsuguninsu bayan tashin hankali a Bama

November 3, 2012

Tun bayan tashe tashen hankullan da suka biyo bayan rikicin addini a kasar Bama ko kuma Miyanmar,kungiyoyin kare hakin bil Adama na nuna damuwarsu a kan lamarin.

https://p.dw.com/p/16cTU
Shofica Belcom, 25, waits with other mothers at a Myanmar Red Cross health clinic near Sittwe, capital of Myanmar's Rakhine state October 14, 2012. Violence erupted in June 2012 between ethnic Buddhist Rakhines and Rohingyas in the northwest Rakhine state, killing at least 77 people and displacing tens of thousands. Belcom and her family have been living in a camp for displaced members of the Rohingya community since June, when the inter-communal violence destroyed her home. The internally displaced persons (IDPs) in Rakhine are accommodated in 40 camps and temporary locations in Sittwe and Kyauktaw townships, with more than 67,700 in nine camps outside Sittwe. Picture taken October 14, 2012. REUTERS/Joe Cropp/International Federation of Red Cross/Handout (MYANMAR - Tags: POLITICS) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Hoto: Reuters

Kungiyar 'yan gudun hijira ta duniya ta bayyana matuƙar damuwarta bisa ga yadda hukumomin ƙasar Bama ko kuma Miyanmar suka fuskanci matsalar 'yan gudun hijiran yankin Rahkine a yammacin ƙasar bayan rikicin addinin da ya ɓarke mako ɗaya da ya shuɗe.
Rahotanni dai sun bayyana cewar sama da mutane 140 ne suka rasa rayukansu sakamakon tashe tashen hankulan da suka biyo bayan rikicin addini tsakanin mabiya addinin Budah da kuma musulmai a kasar inda hasali ma aka goge wani garin musulmin kwata kwata daga doron ƙasa. Dama dai Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana musulman Bama a matsayin jama'an da ta fi fuskantar tsangqwama a duniya. An nunar cewa mutane kimanin 1200 suka ƙaura wa matsugunansu bayan tashin hankalin na addini.

Mawallafi: Issoufou Mamane
Edita : Mohammad Nasiru Awal