1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mozambik na ci gaba da samun tallafi

March 31, 2019

Kasar Mozambik na ci gaba da karbar agaji daga kasashe, daidai lokacin da cutar kwalara ke yaduwa a birnin Beira da ya fuskanci mahaukaciyar guguwa.

https://p.dw.com/p/3Fynb
Mosambik Rotes Kreuz bei den Opfern des Zyklons Idai
Hoto: picture-alliance/AP Photo/D. Onyodi

Kasar China ta aika da kwararrun likitoci birnin na Beira, yayin da wasu masu aikin agaji suka yi ta feshin magungunan yaki da cutar kwalara a ranar Lahadi.

Jami'ai sun ce sama da mutum 270 ne cutar ta kama, koda yake babu rahoton rasa rai da aka ji kawo yanzu.

Sama da mutum 500 ne aka tabbatar da mutuwarsu a hukumance, sakamakon guguwar mai suna Idai da ta afka wa yankin makonni biyun da suka gabata. Wasu 250 ma sun mutu a kasashen Zimbabuwe da Malawi.

Hukumar Lafiyar ta Duniya WHO, ta ce a gobe Litinin za a sami alluran rika-kafin cutar akalla dubu 900.