Rikicin siyasar Venezuela ya dauki hankalin kungiyar EU
January 31, 2019Talla
A ranar Larabar data gabata ne shugaban kasar Amirka Donald Trump ya gargadi Amirkawa da kada su kuskura su sanya kafarsu a kasar Venezuela har sai an warware takaddamar siyasa a kasar, bayan da wasu daga cikin kasashen Turai suka amince da jagoran adawar Venezuela a matsayin shugaban kasa na riko kamar yadda ya bayyana kansa.