1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari a kan sojojin ketare a arewacin Mali

Zainab Mohammed Abubakar
November 30, 2020

Mayakan da ke da alaka da kungiyar al-Qaeda sun kai harin rokoki sansanonin sojojin kasashen ketare da ke garuruwan arewacin Mali na Menaka da Gao da Kidal.

https://p.dw.com/p/3m2hS
Mali Soldaten ARCHIV
Hoto: picture-alliance/dpa

Majiyar sojin Malin da ta ruwaito harin harin na wannan Litinin, ta kara da cewar ba kasafai ake ganin irinsa ba a lokaci guda kuma a wurare daban daban.

Mai magana da yawun rundunar sojin faransa da ke sa jami'ai sama da dubu biyar a Sahel Thomas Romiguier ya bayyana cewar, harin ya ritsa da ginin MDD da ke Kidal wadda ke kusa da sansanin sojin Faransan.

Kasar ta yankin yammacin Afirka dai na fama da matsalolin tsaro daga hare haren mayakan da ke kiran kansu na "Jihadi", rikicin da ya samo tushe daga arewaci kuma sannu a hankali ya bazu zuwa kasashe makwabta na Burkina Faso da Nijar.