1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

MDD ta ce an halaka mutane dubu goma sha biyar a Sudan

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
January 23, 2024

Majalisar Dinkin Duniyar na kokawa da irin munin take hakkin bil'adama a kasar, tun bayan fara yakin a cikin watan Afrilun 2023, tare da raba miliyoyin mutane da gidajensu

https://p.dw.com/p/4bZcv
Hoto: AFP/Getty Images

Majalisar Dinkin Duniya ta ce wani rahotonta ya gano cewa an halaka mutane dubu goma zuwa dubu goma sha biyar a garin El Geneina kadai na yankin Darfur da ke kasar Sudan, tun bayan barkewar rikici tsakanin dakarun sojin kasar karkashin Janar Abdel Fattah al-Burhan, da na RSF da ke karkashin tsohon mataimakinsa  Mohamed Hamdan Dagalo.

Karin bayani:Sudan ta fice daga kasashe membobin kungiyar Igad

Kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya rawaito Majalisar Dinkin Duniyar na kokawa da irin munin take hakkin bil'adama a kasar, tun bayan fara yakin a cikin watan Afrilun bara, tare da raba miliyoyin mutane da gidajensu.

karin bayani:Fatan tattaunawa don kawo karshen rikicin Sudan

Rahoton ya nuna cewa kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya na nazartar batun, tare da duba yiwuwar kakabawa Sudan din takunkumi a kan cin zarafin 'dan adam, da suka hada da fyade da muzgunawa iri-iri.