MDD ta bukaci tsara rigakafin corona
February 17, 2021Talla
Majalisar ta yi gargadin cewa rashin daidaito wajen samun maganin na iya jefa duniya cikin hadari.
Ministocin harkokin waje da suka halarci taron da aka gudanar a karon farko ta yanar Gizo karkashin jagorancin Birtaniya sun baiyana cewa wannan hakki ne da ya rataya a wuyan kasashen duniya baki daya.
Sakataren Majalisar Dinkin Duniyar Antonio Guterres ya nuna damuwa cewa kasashe 10 ne kacal daga cikin kasashe 130 suka aiwatar da 75 cikin dari na allurar rigakafin ya zuwa yanzu.