1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta rantsar da alkalai mata 98

Abdul-raheem Hassan
October 19, 2021

Babban alkali a kasar Masar, ya rantsar da mata 98 a matsayin lauyoyin gwamnati a karon farko bayan da matan suka sha yin zargin nuna musu wariya.

https://p.dw.com/p/41sAh
Ägypten Frauen Demonstration Dezember 2011
Hoto: dapd

An rantsar da matan su kusan 100 a birnin Alkahira watanni kadan bayan da Shugaban kasar Abdel Fattah el-Sissi ya kirayi mata su shiga rukunin lauyoyin kare gwamnati.

A shekarar 1946, aka kafa hukumar shari'a mai zaman kanta da ke kula da rigingimun tare da yin bitar daftarin dokoki da yanke shawara da kwangilolin da suka shafi gwamnati.