1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar za ta maida huldar jakadanci da Libya

Ahmed Salisu
February 16, 2021

Masar ta ce ta fara shirin bude ofishin jakadancinta da ke birnin Tripoli na kasar Libiya a karon farko cikin shekaru shiddan da suka gabata.

https://p.dw.com/p/3pSE0
Ägypten: Präsident  Abdel Fattah al-Sisi
Hoto: Getty Images/AFP/J. Macdougall

Wannan shiri na bude ofishin da aka fara yinsa ya biyo bayan tattaunawa da aka yi tsakanin jami'an kasashen biyu a jiya Litinin da kuma yau Talata kamar yadda kamafanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.

Masar na daga cikin kasashen da ke kan gaba wajen ba da goyon baya ga Janar Khalifa Haftar da a baya yake da gabashin kasar, sai dai ga alama ta sassauto daga wannan matsayin bayyan da aka samu amincewar girka gwamnati a Libiya wadda ta samu karbuwa daga bangarorin kasar da ke gaba da juna.