Majalisar Dinkin Duniya za ta tura tawagar bincike el-Fasher
November 15, 2025
Talla
Matakin dai ya biyo bayan ta'asar cin zarafin fararen hula da aka ruwaito sojojin da ke rikici da sojojin Sudan sun tafka.
Shugaban hukumar Kare Hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, Volker Turk, ya ce laifukan da aka aikata a kwanakin baya-bayan nan a el-Fasher sun munana matuka.
Ya kuma yi gargadin karuwar tashe-tashen hankula a yankin Kordofan da ke tsakiyar kasar Sudan, wanda tuni wasu rahotanni ke bayyana kazantar lamura a yankin.
Yankin Kordofan dai ya kunshi jihohi uku kuma ya kasance matsuguni a tsakanin yankunan yammacin Darfur na karkashin ikon dakarun RSF da kuma jihohin da ke hannun sojoji a yankin gabashin kasar.
Karin Bayani: Dakarun RSF a Sudan amince da kudurin sulhu