Libiya na kai hari a kan 'yan adawa
November 25, 2014Talla
Shafin sadarwa na Internet din Firaminista Abdullah al-Thinni ya ruwaito shi yana mai cewa sojojin saman kasar suka kai hari a filin sauka da tashin jiragen sama da ke birnin na Tripoli. Bayanin na Thinni na zuwa ne bayan da jakadan Majalisar Dinkin Duniya na musamman a Libiyan Bernadino Leon ya bukace shi da ya kawo karshen hare-haren da sojojin gwamnati ke kaiwa ta sama da jiragen yaki a kan 'yan adawa.
Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Mohammad Nasiru Awal