1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Saka hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Libiya

January 13, 2020

Bangarorin da ke rikici da juna a kasar Libiya sun amince da yarjejeniyar zaman lafiya domin kawo karshen rikici a kasar da ke yankin arewacin Afirka.

https://p.dw.com/p/3W9HA
Libyen Fortschritte bei Verhandlungen über Waffenstillstand ARCHIV
Hoto: picture-alliance/Photoshot/A. Salahuddien

A wannan Litinin manyan bangarorin da ke rikici da juna a kasar Libiya, sun saka hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a birnin Moscow na kasar Rasha, kamar yadda jami'an diflomasiyya ta kasar Rasha ta tabbatar. Kasashen Rasha da Turkiyya suka taimaka aka kulla yarjejeniyar. Tun a wannan Lahadi da ta gabata aka fara aikin da ita bisa wani matakin kawo karshen rikici da ya dagula kasar da ke yankin arewacin Afirka.

Yayin da a daya hannu kasar Jamus ta bayyana shirin daukan nauyin taro kan samar da zaman lafiya a kasar ta Libiya tsakanin bangarorin da ke rikicin a ranar 19 ga wannan wata na Janairu.