Za a ji yadda ruwan sama da ake tafkawa a Côte d' Ivoire ya sa hukumar CAF dage gasar kwallon kafa ta kasashen Afirka. Akwai rawar da 'yan matan Kamaru suka taka a wasansu na farko na AFCON rukunin mata. Su kuwa 'yan matan Kamarun sun yi abin da ake dangantawa da babu yabo babu fallasa yayin da Tunisiya da Maroko suka nuna bajinta a AFCON.