1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kyanda ta kashe dubban rayuka a Kwango

December 5, 2019

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta ce akalla mutum dubu biyar ne cutar kyanda ta hallaka a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango a bana kadai, kuma galibinsu kananan yara.

https://p.dw.com/p/3UIET
Indonesien Rund hundert Masern-Tote in Papua  befürchtet
Hoto: Getty Images/AFP/Y. Muhammad

Hukumar ta lafiya ta danganta karancin alluran riga kafi da kuma abinci a matsayin manyan dalilan da suka taimaka wa karuwar mace-macen a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwangon.

Abin kuma ya fi shafar mazauna arewacin lardin Kivu ne da ke fama da matsalar Ebola. Akwai mutane sama da miliyan biyu da ke bukatar alluran na riga kafi a yankin. 

Sai dai aikin na fuskantar matsaloli a yankin saboda hare-haren da ake kaiwa kan jami'an lafiya da kuma na agaji.