1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani Pasto ya rasa ransa sakamakon kamuwa da cutar Ebola

Abdoulaye Mamane Amadou MNA
July 16, 2019

Mutumin farko da ya harbu da cutar Ebola a yankin Goma na Jamhuriyar Demukuradiyyar Kwango ya rasu a daidai lokacin da ake kan hanyar mayar da shi cibiyar da ke karbar masu dauke da cutar a garin Butembo.

https://p.dw.com/p/3MAGc
Ebola im Kongo
Hoto: picture-alliance/dpa/Al Hadji Kudra Mliro

Mutumin da ya rasu ne kwanaki bayan an gano da ya kamu da cutar. Kafin ya rasu mutumin malamin addini ne da ya sha yin wa'azi tare da yin mu'amala da jama'a da dama kafin cutar ta yi sanadiyyar mutuwarsa.

Mutuwar Paston ta haifar da fargaba ga al'ummar yankin na Goma, daya daga cikin yankunan kasar mafi yawan al'umma a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango. Sai dai gwamnan yankin ya bukaci jama'a da su kwantar da hankulansu tare da kasancewa a cikin tsafta.

Cutar ta Ebola ta hallaka akalla mutane 1660 sakamakon kamuwa da ita a yankunan kasar dabam-dabam.