1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Brexit: 'Yan majalisa za su kada kuri'a kan ficewa daga EU

Ramatu Garba Baba
October 19, 2019

Al'umma na shirin yin tattaki a birnin Landan a yayin da 'yan majalisa ke shirin kada kuri'ar amincewa da yarjejeniyar Firaiminista Boris Johnson kan ficewar Britaniyya daga Kungiyar EU.

https://p.dw.com/p/3RYb6
UK Brexit | Parlament
Hoto: AFP/HO

'Yan majalisar dai za su kada kuri'an bisa nuna amincewa ko akasin hakan da daftarin na mista Johnson. Firaiministan da ya dage kan ficewar kasar koda ba da yarjejeniya ba, yana neman goyon bayan 'yan majalisar a matakin da zai bai wa Britaniyyan damar raba gari da kungiyar ba tare da an fuskanci tarnaki ba. A ranar talatin da daya ga wannan watan na Oktoba, wa'adin ficewar ke cika.