1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karuwar kamen masu mu'amalar jinsi dayaa Kamaru

Binta Aliyu Zurmi
April 15, 2021

Jami'an tsaro a jamhuriyyar Kamaru sun kara kame wasu mutane masu mu'amala ta jinsi daya.

https://p.dw.com/p/3s2jt
Namibia Gay Pride Parade 2016
Hoto: picture-alliance/NurPhoto/O. Rupeta

 A cewar kungiyar kare hakkin bil Adama ta Human Right Watch daga watan Fabarairu zuwa yanzu an kama sama da mutum 24 a kasar. Lamarin da ta yi tir da shi.

Kungiyar ta ce ta sanar da hukumomin da ke da ruwa da tsaki a kan rahoton ta na yadda ake musgunawa wadannan mutanen da ke neman jinsi guda amma kama daga ma'aikatar shari'a da jami'an 'yan sanda babu wanda ya ce mata uffan a kan wannan lamarin.

Kamaru dai kamar sauran kasashe a nahiyar Afirka mu'amala ta masu neman jinsi daya na samun tirjiya daga al'umma da ma hukumomi, wanda idan aka gurfanar da mutum a gaban kuliya zai iya samun shekaru har biyar a gidan gyara hali.