Kotu a Isra'ila ta dage haramcin kungiyoyin agaji a Gaza
February 27, 2026
Talla
A karshen shekarar 2025 ne Isra'ila ta dakatar ayyukan kungiyoyin agajin saboda karewar rejistar su, kungiyoyin da matakin ya shafa sun hada da Doctors Without Borders wato likitocin na gari na kowa da kungiyar Oxfam da hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Norway da kuma kungiyar CARE.
Gwamnatin Isra'ila ta kafa wa kungiyoyin sharadin gabatar da sunayen Falasdinawa da ke musu aiki kafin a sabunta rejistar kungiyoyinsu don cigaba da ayyukan agaji. Dakatar da ayyukan kungiyoyin ya jefa rayuwar fararen hula da dama a cikin hatsari sakamakon rashin magunguna da abinci.