1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta soke zabe a Malawi

February 3, 2020

Bayan korafe-korafe da kuma watanni na zanga-zanga, kotu a Malawi ta soke zaben kasar da aka yi a bara sakamakon saba ka'idojin zabe da ta bankado cikin ayyukan hukumar zabe.

https://p.dw.com/p/3XDjk
Malawi, Lilongwe: Proteste gegen die Regierung
Hoto: Getty Images/AFP/A. Gumulira

Kotun tsarin mulki a Malawin ce dai ta soke zaben kasar da ya bai wa Shugaba Peter Mutharika nasara a watan Mayun shekarar da ta gabata, saboda kura-kuran da ta ce an tafka. Alkalin kotun Healey Potani, ya ce sakamakon hakan dole ne a sake zabe a Malawin.

Manyan 'yan takarar hamayya a zaben kasar ne dai suka kalubalanci nasarar Shugaba Mutahrika, wanda ya sha gabansu da karamin rinjaye.

Kotun ta lura da gyare-gyare kan takardun kada kuri'a da suka fi miliyan daya da budbu 400.

Watanni da dama ne dai aka kwashe ana ta zanga-zanga a Malawin saboda rashin amincewar da aka nuna dangane da sakamakon.