1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun sace wata baturiya a kasar Kenya

Ramatu Garba Baba
November 21, 2018

Wasu 'yan bindiga 8 sun sace ma'aikaciyar da ke aikin koyarwa a wata makarantar gaba da firamare da ke daf da gabar ruwan kasar Kenya, mutum biyar cikinsu har da kananan yara sun jikkata a sanadiyar harbe-harben bindiga.

https://p.dw.com/p/38fWL
Bangladesch Japaner Mord Kunio Hoshi
Hoto: picture-alliance/dpa/Stringer

 

Matar mai suna Sylvia Constanza Romano, 'yar shekaru 23 da haihuwa ta na aiki ne a karkashin kungiyar Africa Milele Onlus da ke a yankin Kilifi. Wani ganau mai suna Ronald Kazungu Ngala, ya ce a kan idanunsa suka diran ma makarantar suka kuma nemi ya nuna musu inda matar ta ke. Hukumomin Kenya sun ce suna aiki tukuru don ganin an kubuto matar a raye.

Mayakan jihadi na El-Shabab na kasar Somaliya sun yi kaurin suna a sace mutane musanman Turawa daga wannan yankin ko don neman kudin fansa.