Kasashen Duniya na ganawa a Amirka
September 19, 2016Talla
A taron dai ana sa ran cewar Babban sakataren MDD Ban Ki Moon wanda zai ajiye mukaminsa a ranar 31 ga watan Disamba da shugaba Barack Obama na Amirka da ke kammala wa'adin mulkinsa a watan Janairu, za su yi jawabinsu na karshe a gaban majalisar a yayin da firaministan Birtaniya Theresa May za ta yi fitowarta ta farko tun bayan dare kujera mulki a kasa da watanni uku da suka gabata bayan ficewar kasarta daga Kungiyar tarayyar Turai EU.