1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina da Mali za su karfafa matakan tsaron iyakokinsu

Abdoulaye Mamane Amadou
August 27, 2019

Mali da Burkina Faso sun bayyana anniyarsu ta sake karfafa matakan soja kan iyakokinsu kwanaki bayan wani mumunan harin ta'addanci da mayakan jihadi suka kai a Burkina Faso da yayi sanadiyar mutuwar sojoji 24

https://p.dw.com/p/3OYZj
Burkina Faso Sicherheitskräfte
Hoto: Getty Images/AFP/A. Ouoba

A yayin da yake ganawa da firaministan Burkina Faso Christophe Dabiré a yammacin jiya, ministan tsaron Mali Janar Ibrahima Dembélé, ya ce tuni bangarorin kasashen biyu suka fara kaddamar da tsaron iyakokinsu na hadin gwiwa, a wani yunkuri na kawo karshen hare-haren ta'addancin da ke addabar kasashen biyu da kuma suka yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.