Kamaru: Wani shugaban gunduma ya bace
February 12, 2018Talla
An kashe Jandarmomin uku ne a garin Kembon a yankin Kudu maso yammacin kasar, inda aka samu wasu hare-hare nan da can kafin a shayo kan matsalar a cewar Kanal Didier Badjeck mai magana da yawun rundinar sojojin kasar ta Kamaru. A yankin Batibo kuwa da ke Arewa maso yammacin kasar inda ake magana da turancin Ingilishi, an tarar da motar shugaban gundumar Namata Dientg a kone kurmus, sai dai kuma shi ba'a san inda ya shiga ba har ya zuwa yammacin ranar Lahadi a cewar dan majalisar yankin na Batibo Joseph Mbah-Ndam. Tun farkon rikicin yankin da ake magana da turancin Ingilishi a Kamaru a shekara ta 2016 kawo yanzu, an samu rasuwar jami'an tsaro 26 kaman yadda gwamnatin kasar ta sanar.