1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan awaran sun ce ba za su halarci taron sulhun ba

Mohammad Nasiru Awal AH
September 12, 2019

Tun kimanin shekaru uku da suka gabata ake fama da tashin hankalin na Kamaru wanda ake ganin Shugaba Paul Biya ya yi sako-sako amma yanzu ya yi alkawarin shirya wani taron tattaunawa na kasa.

https://p.dw.com/p/3PV9z
Kamerun Präsident Paul Biya
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

Bisa al'ada dai sau uku a shekara Shugaban Kasar Kamaru Paul Biya yake jawabi ga 'yan kasar. Amma rikicin da aka kwashe tsawon shekaru uku ana yi da 'yan aware a yankunan masu amfani da harshen Ingilishi ya sa shugaban ya sanar da cewar za a gudanar da babban taron tattaunawa domin samun bakin zaren warware rikicin a karshen wannan wata na Satumba. Sai dai an samu martani mabambamta kan jawabin na Shugaba Biya. Simon Ntonga mai nazarin harkokin siyasa ne  a Kasar ta Kamaru da ya yi fatan cewa shugaban zai cika alkawarin da ya dauka. Ya ce: "A karon farko ina iya cewa mun gano cewa da gaske shugaban kasar yake a kan abin da ya fada da kuma yake tunani, zai tabbatar da dukkan alkawuran da ya yi a cikin sanarwar."