1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sako dalibai 79 da aka sace daga wata makaranta

Ramatu Garba Baba
November 7, 2018

An sako dukkanin dalibai 79 da wasu 'yan bindiga suka sace daga wata makaranta da ke a yankin Bamenda na masu anfani da turancin Ingilishi a Kamaru.

https://p.dw.com/p/37ouh
Kamerun Bamenda Schüler entführt
Hoto: Reuters/B. Eyong

Minisitan yada labarai na kasar Kamaru, Issa Bakary Tchiroma, ya ce an sako 'yan makaranta nan saba'in da tara da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a shekaranjiya Litinin. Ministan dai bai yi wani karin bayani kan hanyoyin da gwamnati ta bi kafin a dawo da yaran ba. Sai dai ya ce har yanzu basu da labari kan malaman da aka yi garkuwa da su tare da wadannan yaran.

Wasu da ake zargin 'yan aware masu fafutukar ballewar daga Kamaru, su suka diran ma makarantar sakandaren da ke a yankin Bamenda, inda suka yi awon gaba da daliban tare da malaman nasu. Wannan shi ne karon farko da kasar mai fama da rikicin masu neman an ballen, ke fuskanta wannan matsala ta yin garkuwa da 'yan makaranta.